HomeSashen HausaMatsalolin Tsaro Za Su Zama Tarihi A Shekarar 2026– Shugaba Tinubu

Matsalolin Tsaro Za Su Zama Tarihi A Shekarar 2026– Shugaba Tinubu

-

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta ƙara zurfafa haɗin gwiwa da ƙasashen Duniya a shekarar 2026, domin murƙushe dukkan barazanar tsaro da ke barazana ga rayuka, dukiyoyi da cikakken ikon ƙasar Najeriya.

‎Shugaban ya bayyana hakan ne a jawabin saƙon sabuwar shekarar 2026 da ya gabatar ga ’yan Najeriya, inda ya jaddada cewa ba za a samu ci gaban tattalin arziki mai ɗorewa ba sai an tabbatar da tsaro da zaman lafiya.

 

‎Tinubu ya ce, Najeriya na fuskantar barazanar ’yan ta’adda da ’yan fashi, amma gwamnati na ɗaukar matakai masu ƙarfi, ciki har da hare-haren haɗin gwiwa da abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa, musamman Amurka, domin raunana ƙungiyoyin ta’addanci.

‎“A ranar 24 ga watan Disamba, an kai hare-hare masu ƙarfi kan sansanonin ’yan ta’adda a wasu sassan Arewa maso Yamma,” inji shugaban.

 

Nigerian Post ta bibiyi cewa, ‎Tunibu ya jaddada cewa, rundunonin tsaro za su ƙarfafa musayar bayanai da daidaita ayyuka da ƙasashen waje a 2026, tare da tabbatar da kare rayuka da dukiyoyin ’yan ƙasa.

Haka kuma, ‎game lda tsarin tsaro, Tinubu ya nuna goyon bayansa ga ’yan sanda na jihohi, tare da tanadin tsarin doka da kula da masu tsaron dazuka.

‎A ɓangaren tattalin arziki, shugaban ya ce 2026 za ta zama shekarar bunƙasar tattalin arziki, inda za a hanzarta shirin Renewed Hope Ward Development Programme da nufin samar da ayyukan yi ga ’yan Najeriya miliyan 10.

‎Ya kuma tabbatar da ci gaba da manyan ayyukan more rayuwa, tare da kira ga ’yan Najeriya da su bada gudummawar su wajen gina ƙasa.

‎A ƙarshe, Tinubu ya yi wa ’yan Najeriya fatan sabuwar shekara mai cike da zaman lafiya, tsaro da ci gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎An Cafke Wani Mutum Da Zargin Sayar Da Jaririn ‘Yar’ uwarsa Naira Miliyan 2 a Legas

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta kama wani mutum mai shekaru 30 da haihuwa bisa zargin sayar da jaririn ‘yar uwarsa mai wata daya kacal...

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi Hukumar tsaron farin kaya ta DSS sun damƙa matashiya Walida Abdullahi Ibrahim ga Gwamnan Jihar Jigawa,...

Most Popular