HomeSashen HausaHukumomin Saudiyya sun amince da binne Aminu Dantata a Madina

Hukumomin Saudiyya sun amince da binne Aminu Dantata a Madina

-

Gwamnatin kasar Saudiyya ta amince da binne fitaccen dan kasuwar nan na Najeriya, Aminu Dantata a birnin Madina mai alfarma.

Babban sakatare mai zaman kansa, Mustapha Junaid, ya tabbatar da faruwar lamarin a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

A cewarsa, za a dauki gawar mamacin ne daga Abu Dahabi ta ƙasar Dubai zuwa ƙasar Saudiyya.

Ana sa ran za a yi jana’izar ne a safiyar ranar Litinin a birnin Madina.

Alhaji Aminu Dantata, na ɗaya daga cikin hamshakan attajiran Najeriya, ya rasu a Dubai bayan ya yi fama da doguwar jinya ya rasu yana da shekaru 94 a Duniya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Tsofaffin Ma’aikatan FRCN, Sun Shirya Jagorantar Zanga-zanga Zígídír, Kan Ƙin Biyansu Haƙƙinsu A Najeriya

A wani rahoto da Nigerian Post ta samu daga Aminiya, an tabbatar da cewa, tsofaffin ma’aikatan (FRCN) Federal Radio Corporation of Nigeria (FRCN) sun ce...

Mace Mai Juna Biyu Ta Rasa Ranta Bayan Ma’aikaci Ya Ki Karɓar Transfer Don Biyan Kudin Iskar Numfashi A Asibitin Turai Katsina

Mace Mai Juna Biyu Ta Rasa Ranta Bayan Ma’aikaci Ya Ki Karɓar Transfer Don Biyan Kudin Iskar Numfashi A Asibitin Turai Katsina Wata mata mai juna...

Most Popular