HomeSashen HausaGwamna Abba Kabir Yusuf ya jagoranci tawogar Kano da Jigawa zuwa halartar...

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jagoranci tawogar Kano da Jigawa zuwa halartar jana’izar Dantata a Madina

-

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya tashi daga Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano, inda yake jagorantar wata babbar tawaga domin halartar jana’izar fitaccen attajiri kuma dattijon kasa, marigayi Alhaji Aminu Alhassan Dantata, a birnin Madina mai alfarma, da ke Kasar Saudiyya.

Marigayin ya rasu da safiyar Asabar a birnin Abu Dhabi na Hadaddiyar Daular Larabawa.

Wannan bayanin na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar.

Tawagar tana dauke da Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II, Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Umar Namadi, tsohon gwamnan Jigawa Barr. Ali Sa’ad Birnin Kudu, da wasu manyan jami’an gwamnati da fitattun dattawan jihar.

Da ya ke jawabi kafin tafiya daga filin jirgin sama, Gwamna Yusuf ya bayyana marigayi Dantata a matsayin “uba ga mutane da dama, wanda kyautatawarsa da kishinsa ga dan Adam suka wuce kima da iyaka.”

Gwamnan ya jaddada cewa halartar tawagar Kano a jana’izar da za a gudanar a Madina na nuni da irin girmamawa da godiya da al’ummar Kano ke da ita ga marigayin da irin gudummawar da ya bayar a rayuwarsa.

Ana sa ran jana’izar za ta ja hankalin wakilan jihohi da na gwamnatin tarayya, ‘yan uwa da abokan arziki, masana addini da masoya daga sassa daban-daban na duniya, dukkansu domin yin addu’a da neman gafara ga marigayin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Kanwan Katsina Advocates Establishment of FM Stations Across 3 Senatorial Zones Katsina

The Kanwan Katsina District Head of Ketare, Alhaji Usman Bello Kankara mni, has emphasized the need for continuous training and capacity building for journalists, particularly...

‎Ganduje Ba Shi da Alhakin Sace Dadiyata – Shehu Sani

Tsohon dan majalisar dattawa mai wakiltar mazabar Kaduna ta Tsakiya a Majalisar Dattawa ta 8, Shehu Sani, ya karyata zargin da tsohon gwamnan Jihar Kaduna,...

Most Popular