HomeSashen HausaPDP da APC Sun Fusata Kan Hukuncin Kotun Kanada Na Dangantasu Da...

PDP da APC Sun Fusata Kan Hukuncin Kotun Kanada Na Dangantasu Da Ta’addanci

-

Wata kotun tarayya a ƙasar Kanada ta haifar da cece-kuce bayan da ta danganta manyan jam’iyyun siyasa na Najeriya, Peoples Democratic Party (PDP) da All Progressives Congress (APC), da abubuwan da ta bayyana a matsayin ayyuka masu kama da ta’addanci.

Hukuncin ya samo asali ne daga shari’ar wani ɗan Najeriya mai neman mafaka, Douglas Egharevba, wanda kotun ta ƙi buƙatarsa bisa kasancewarsa tsohon memba na PDP da APC.

PDP ta yi watsi da hukuncin tana mai cewa babu tushe kuma an yi shi ne da son zuciya. Ita kuwa APC ta ce kotun ba ta da ikon ayyana jam’iyya a matsayin ƙungiyar ta’addanci, tana mai jaddada cewa jam’iyyarta ta dimokuradiyya ce.

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayyana hukuncin a matsayin abin da zai iya haifar da illa ga dangantakar diflomasiyya tsakanin Najeriya da Kanada, yayin da masana suka yi gargadin cewa wannan lamari na iya kawo kalubale ga tsarin dimokuradiyya a Afirka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Gwamnan Katsina Ya Zama Abin Koyi Ga Sauran Jihohin Najeriya— Inji Kashim Shettima

Mataimakin shugaban ƙasar Najeriya, Sanata Kashim Shettima, ya bayyana cewa, Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Raɗɗa, ya zama abin koyi idan akai duba da...

Budurwa Ta Hallaka Kanta A Jihar Borno Bayan Tilasta Ma Ta Auren Dole

Wata matashiya ta kashe kanta a karamar hukumar Gubio ta jihar Borno, bayan mahaifinta ya tilasta mata aure da ɗaya daga cikin abokansa.   Shafin jaridar Zagazola...

Most Popular