HomeLabaraiJami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Kungiyar Ansaru

Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Kungiyar Ansaru

-

Mai Ba wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro na Ƙasa (NSA), Malam Nuhu Ribaɗu, ya bayyana cewa jami’an tsaro sun samu gagarumar nasara ta hanyar cafke manyan shugabannin kungiyar ta’addanci ta Ansaru.

Ribaɗu ya bayyana wa ’yan jarida a Abuja cewa aikin ya gudana tsakanin watan Mayu zuwa Yuli, inda jami’an tsaro suka yi amfani da sahihan bayanan leken asiri wajen ƙaddamar da farmaki.

Ya ce wannan aiki ya rusa shugabancin ƙungiyar Ansaru mai alaƙa da Al-Qaeda, tare da bayyana shi a matsayin “mummunan rauni mafi girma da aka taɓa yi musu a tarihin ƙungiyar.”

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, NSA ya ƙara da cewa rundunar sojoji, hukumomin leƙen asiri da sauran jami’an tsaro ne suka aiwatar da wannan aiki na haɗin gwiwa, abin da ya nuna muhimmancin haɗa kai wajen yaƙi da ta’addanci a Najeriya.

Haka kuma, Ribaɗu ya buƙaci kafafen watsa labarai da su ci gaba da hana ’yan ta’adda samun damar amfani da kafafen jarida wajen yaɗa mugayen manufofinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Atletico Knock Out Barcelona to Secure First Semifinal Spot in Eight Years

Atlético Madrid reached the semifinals for the first time since 2017 after knocking out FC Barcelona. Barcelona started the match strongly, with Lamine Yamal and Ferran...

FG Denies ADC Use of Eagle Square for Abuja Convention

The African Democratic Congress (ADC) has said it was denied access to both Eagle Square and the Moshood Abiola National Stadium for its planned national...

Most Popular