HomeSashen HausaSojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen Shugaban ’Yan Bindiga, Kallamu, A Jihar Sokoto

Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen Shugaban ’Yan Bindiga, Kallamu, A Jihar Sokoto

-

Sojojin Rundunar 8 Division ta Najeriya a Sokoto sun samu gagarumar nasarar kawar da fitaccen shugaban ’yan bindiga, Kachalla Kallamu, a yankin Sabon Birni, Jihar Sokoto.

 

An kashe Kallamu ne a wani samame na musamman da sojoji suka gudanar tare da hadin gwiwar ’yan sa-kai a yankin Kurawa, da safiyar Litinin.

 

Kallamu, wanda babban na hannun daman shugaban ’yan bindiga Bello Turji ne, ya kasance daya daga cikin wadanda suka addabi al’ummar Sabon Birni da hare-hare, garkuwa da mutane da kuma tada tarzoma a yankin.

 

Rahotonni sun bayyana cewa an kashe shi ne tare da daya daga cikin manyan masu samar wa Turji da kayan aiki da bayanan sirri, a wani artabu da ya faru da safiyar litinin.

 

Rahotanni sun ce Kallamu, wanda asalinsa daga Garin-Idi a Sabon Birni, ya dawo ne cikin yankin bayan tserewa wani farmaki da sojoji suka kai masa a watan Yunin 2025, inda ake zargin ya shige Kogi domin buya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Light of Hope International Schools Celebrated Cultural Diversity In Katsina  ‎

Light of Hope School katsina, has hosted a colourful first term Annual Cultural Day Celebration showcasing Nigeria's cultural heritage and strengthening unity among students, teachers...

‘Yansanda Sun Cafke Mai Gadi Da Abokinsa Kan Zargin Halaka Tsohuwar Mai Shari A Jihar Delta

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Delta ta tabbatar da kama mutum biyu da ake zargi da hannu a kisan gillar da aka yi wa tsohuwar alkaliyar...

Most Popular