HomeLabarai‎Mataimakin Gwamnan Bayelsa Ya Yanke Jiki Ya Fadi Ana Tsaka Da Aikin...

‎Mataimakin Gwamnan Bayelsa Ya Yanke Jiki Ya Fadi Ana Tsaka Da Aikin Ofis

-

Mataimakin Gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo, ya yanke jiki ya fadi yayin da yake tsaka da gudanar da ayyukansa a ofis ɗinsa da ke Gidan Gwamnati, Yenagoa, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

‎Shaidu daga fadar gwamnati sun ce lamarin ya faru ne ba wani manuniyar cewa yana da wata rashin lafiya, lamarin da ya jefa ma’aikatan ofishin cikin tashin hankali.

‎Rahotanni sun tabbatar da cewa an gaggauta kai Mataimakin Gwamnan zuwa Babban Asibitin Tarayya da ke Yenagoa (Federal Medical Centre) domin kula da lafiyarsa.

‎Duk da cewa hukumomin jihar ba su fitar da cikakken bayanin halin da yake ciki ba tukuna, majiyoyi sun ce likitoci suna ci gaba da aiki tukuru don tabbatar da ya farfaɗo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

CAF Strips Senegal of AFCON 2025 Title, Awards It to Morocco

The Confederation of African Football (CAF) has stripped Senegal of the 2025 Africa Cup of Nations (AFCON) title and awarded it to Morocco. In a statement...

Mutane 23 Sun Mutu, Sama da 100 Sun Jikkata a Harin Bama-bamai a Maiduguri

‎Aƙalla mutane 23 sun mutu, yayin da mutane 108 suka jikkata sakamakon wasu jerin fashewar bama-bamai da suka auku a daren Litinin. ‎ ‎Rundunar ’yan sandan Jihar...

Most Popular