HomeSashen HausaDalilan da su ka sa Ganduje ya yi murabus na shugabancin jam'iyyar...

Dalilan da su ka sa Ganduje ya yi murabus na shugabancin jam’iyyar APC

-

Dalilan da su ka sa Ganduje ya yi murabus na shugabancin jam’iyyar APC

A cikin wani mataki da ya ba da mamaki, Abdullahi Umar Ganduje, Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, ya yi murabus daga mukaminsa nan take.

Ganduje, tsohon Gwamnan Jihar Kano, ya bayyana dalilin neman lafiya a matsayin abin da ya sa ya yanke shawarar sauka daga kujerar, yana mai cewa yana buƙatar mayar da hankali kan lafiyarsa.

Jaridar Premium Times ta rawaito cewa duk da cewa takardai murabus din na sa ta danganta saukarsa da batun lafiya, majiyoyi da ke da masaniya da al’amarin sun nuna cewa, akwai yiwuwar rikici na siyasa a cikin jam’iyyar, wanda hakan ya taka rawa wajen yanke shawarar da ya ɗauka.

An yi hasashen dangantakar saukarsa na ɗaya daga cikin wasu zarge-zargen almundahana da suka shafi harkar kuɗi, inda wasu mambobin jam’iyyar suka bayyana rashin jin daɗinsu kan yawan bukatun kuɗi fiye da kima da ofishinsa ke kakaba wa ya’yan jam’iyyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe...

Most Popular