HomeSashen HausaDalilan da su ka sa Ganduje ya yi murabus na shugabancin jam'iyyar...

Dalilan da su ka sa Ganduje ya yi murabus na shugabancin jam’iyyar APC

-

Dalilan da su ka sa Ganduje ya yi murabus na shugabancin jam’iyyar APC

A cikin wani mataki da ya ba da mamaki, Abdullahi Umar Ganduje, Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, ya yi murabus daga mukaminsa nan take.

Ganduje, tsohon Gwamnan Jihar Kano, ya bayyana dalilin neman lafiya a matsayin abin da ya sa ya yanke shawarar sauka daga kujerar, yana mai cewa yana buƙatar mayar da hankali kan lafiyarsa.

Jaridar Premium Times ta rawaito cewa duk da cewa takardai murabus din na sa ta danganta saukarsa da batun lafiya, majiyoyi da ke da masaniya da al’amarin sun nuna cewa, akwai yiwuwar rikici na siyasa a cikin jam’iyyar, wanda hakan ya taka rawa wajen yanke shawarar da ya ɗauka.

An yi hasashen dangantakar saukarsa na ɗaya daga cikin wasu zarge-zargen almundahana da suka shafi harkar kuɗi, inda wasu mambobin jam’iyyar suka bayyana rashin jin daɗinsu kan yawan bukatun kuɗi fiye da kima da ofishinsa ke kakaba wa ya’yan jam’iyyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina Police Received 29 New ASPs From The Nigeria Police Academy, Wudil

The Katsina State Police Command has received 29 newly posted Assistant Superintendents of Police (ASPs) from the Nigeria Police Academy, Wudil. Welcoming the officers, the...

Yawancin Fulanin Da Suke Ta’addanci Ba Su Da Addini, Ba Su San Allah Ba– Nasir El Rufa’i ‎

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufa’i, ya bayyana cewa yawancin mutanen Fulani da ake zargi da aikata ta'addanci da kashe kashe a sassa daban...

Most Popular