HomeSashen HausaGwamnatin Katsina Za Ta Farfaɗo da noman Auduga da gina Cibiyar Sarrafa...

Gwamnatin Katsina Za Ta Farfaɗo da noman Auduga da gina Cibiyar Sarrafa Nama

-

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta ƙuduri aniyar farfaɗo da noman Auduga da kuma kafa babbar cibiyar sarrafa Nama a jihar, domin zuba jari daga masu zaman kansu da kuma samar da aikin yi a jihar.

Ya bayyana haka ne yayin da ya karɓi baƙuncin Darakta Janar na Hukumar Binciken Kimiyyar Halitta ta Ƙasa (NBRDA), Farfesa Abdullahi Mustapha, wanda ya zo don ƙulla haɗin gwiwa tsakanin hukumar da kamfanin Dar Al-Halal Animal Farm.

Kamar yadda wakiliyar Nigerian Post ta bibiyi batutuwan Sadiya Sani Sadiq, an shirya haɗin gwiwar ne don gina katafaren matattarar Nama da za ta sanya Najeriya ta shiga sahun ƙasashen da ke fitar da Nama zuwa waje, tare da samar da dubban ayyukan yi a Katsina.

Gwamna Radda ya ce, Manoma da dama sun daina noman Auduga saboda rashin ingantattun iri, inda ya jaddada cewa suna shirin kawo sabbin iri da tallafi don su dawo da darajar Noma.

Ya ƙara da cewa, Noma ne tushen ci gaban tattalin arzikin jihar, kuma gwamnatinsa za ta ci gaba da raba taki da kayan aiki domin tallafa wa Manoma.

Shi ma, Farfesa Mustapha ya jinjina wa Gwamna Radda, bi sa yadda ya ke ba da muhimmanci ga harakokin Noma da Kimiyya, inda ya ce wannan haɗin gwiwa zai taimaka wajen bunƙasa Abinci, rage talauci da haɓɓaka cigaban jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Kanwan Katsina Advocates Establishment of FM Stations Across 3 Senatorial Zones Katsina

The Kanwan Katsina District Head of Ketare, Alhaji Usman Bello Kankara mni, has emphasized the need for continuous training and capacity building for journalists, particularly...

‎Ganduje Ba Shi da Alhakin Sace Dadiyata – Shehu Sani

Tsohon dan majalisar dattawa mai wakiltar mazabar Kaduna ta Tsakiya a Majalisar Dattawa ta 8, Shehu Sani, ya karyata zargin da tsohon gwamnan Jihar Kaduna,...

Most Popular