HomeSashen HausaGwamnatin Katsina Za Ta Farfaɗo da noman Auduga da gina Cibiyar Sarrafa...

Gwamnatin Katsina Za Ta Farfaɗo da noman Auduga da gina Cibiyar Sarrafa Nama

-

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta ƙuduri aniyar farfaɗo da noman Auduga da kuma kafa babbar cibiyar sarrafa Nama a jihar, domin zuba jari daga masu zaman kansu da kuma samar da aikin yi a jihar.

Ya bayyana haka ne yayin da ya karɓi baƙuncin Darakta Janar na Hukumar Binciken Kimiyyar Halitta ta Ƙasa (NBRDA), Farfesa Abdullahi Mustapha, wanda ya zo don ƙulla haɗin gwiwa tsakanin hukumar da kamfanin Dar Al-Halal Animal Farm.

Kamar yadda wakiliyar Nigerian Post ta bibiyi batutuwan Sadiya Sani Sadiq, an shirya haɗin gwiwar ne don gina katafaren matattarar Nama da za ta sanya Najeriya ta shiga sahun ƙasashen da ke fitar da Nama zuwa waje, tare da samar da dubban ayyukan yi a Katsina.

Gwamna Radda ya ce, Manoma da dama sun daina noman Auduga saboda rashin ingantattun iri, inda ya jaddada cewa suna shirin kawo sabbin iri da tallafi don su dawo da darajar Noma.

Ya ƙara da cewa, Noma ne tushen ci gaban tattalin arzikin jihar, kuma gwamnatinsa za ta ci gaba da raba taki da kayan aiki domin tallafa wa Manoma.

Shi ma, Farfesa Mustapha ya jinjina wa Gwamna Radda, bi sa yadda ya ke ba da muhimmanci ga harakokin Noma da Kimiyya, inda ya ce wannan haɗin gwiwa zai taimaka wajen bunƙasa Abinci, rage talauci da haɓɓaka cigaban jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano Wani barawon mota ya kutsa cikin Gidan Gwamnatin Kano da sanyin safiyar Litinin ya kuma...

‎Yansanda Sun Kama Masu Aikata Laifuka Daban-daban, Sun Ceto Mutane 47 da Aka Yi Garkuwa da Su a Jihar Katsina

Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Katsina ta bayyana cewa ta samu nasarori masu yawa a yakin da take yaki da laifuka, ciki har da kama mutanen...

Most Popular