HomeSashen HausaPDP Ta Yi Tur Da Kamen Da Aka Yi Ma Tsohon Gwamna...

PDP Ta Yi Tur Da Kamen Da Aka Yi Ma Tsohon Gwamna Aminu Waziri Tambuwal

-

Jam’iyyar PDP a jihar Sokoto ta yi Allah-wadai da kamawa tare da tsare tsohon gwamnan jihar, Sanata Aminu Waziri Tambuwal, tana zargin jam’iyyar APC da yunƙurin jefa dimokuraɗiyyar ƙasar cikin rudani.

A cewar wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran PDP na jihar, Hassan Sahabi Sanyinnawal, ya fitar a yau Talata, wannan kamen na daga cikin shirin cin zarafi da murƙushe ‘yan adawa a Najeriya.

“Ana wannan kame-kamen ne a daidai lokacin da ake ƙoƙarin samar da haɗakar jam’iyyun adawa a ƙasar domin fuskantar zaɓe mai zuwa. Wannan mataki ba zai hana mu ci gaba da ƙoƙarin kawo sauyi ba,” in ji Sanyinnawal.

Ya kuma yi kira ga Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) da ta daina zama “karen farauta” na gwamnatin tarayya wajen cin zarafin jam’iyyun adawa.

Tun da farko, EFCC ta gayyaci Sanata Tambuwal inda ya isa ofishinta a ranar Litinin domin amsa tambayoyi. Rahotanni sun tabbatar da cewa bayan ya amsa gayyatar, hukumar ta tsare shi bisa zargin almundahanar kuɗi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Hukumar NSCDC A Katsina Ta Yi Sabon Shugaba

Hukumar Tsaro ta NSCDC reshen Jihar Katsina ta samu sabon kwamanda bayan sauyin shugabanci da ya gudana a ranar Litinin, 22 ga watan Satumba, 2025.   A...

Gwamnatin Jihar Katsina Ta Horas Da Malamai 250 Da Faransifal 50, Don Inganta Ilmin Jihar

Ma’aikatar Ilimi a Matakin Farko da na Sakandire a jihar Katsina, haɗin gwiwa da Majalisar Turai (British Council), ta ƙaddamar da wani muhimmin shirin horaswa...

Most Popular