HomeSashen HausaYan Wasan Katsina Football Acadamy 5 Sun Samu Shiga Babbar Kungiyar Kwallon...

Yan Wasan Katsina Football Acadamy 5 Sun Samu Shiga Babbar Kungiyar Kwallon Ƙafa Ta Katsina United

-

Makarantar koyar da Wasan Kwallon kafa ta Katsina Football Academy ta Taya Yan Wasan ta biyar (5) murnar samun girma zuwa Babbar Kungiyar Kwallon kafa ta Katsina United.

Bayanin hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Daraktan wasanni na Makarantar Shamsuddeen Ibrahim ya fitar biyo bayan da Babbar Kungiyar Kwallon kafar ta katsina United ta fitar da jerin sunayen Yan Wasa Yan asalin Jihar Katsina da ta dauka ga bannin fara Gasar Kakar Wasanni ta NPFL zango na 2025/2026.

Sanarwar ta ambato Daraktan kwalejin yana bayyana daukar Yan Wasan Makarantar ta katsina football academy amatsayin wata nasara a rayuwar su ta Kwallon kafa, inda ya bukace su dasu kasan ce jakadu na gari a yayin da suke a Babbar Kungiyar Kwallon kafar ta Jiha.

Da ya ke yima Yan Wasan fatan alkhairi, Shamsuddeen Ibrahim ya Kuma Yi Kira garesu dasu kara zage damtsi, su Kuma Yi aiki tukuru a yayin da zasu tun Kari Babbar Gasar Kwallon kafa ta Kasar Nigeria.

Yan Wasan da suka samu nasarar shiga Kungiyar Kwallon kafar ta katsina United sun hada da Usman Abdullahi, Ahmad Nasir, Umar Yusuf, Abubakar Hassan da Kuma Kabir Muhammad Kabir.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Nijeriya Ta Musanta Zargin Leken Asiri Kan Jirginta Da Ke Burkina-Faso

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF) ta karyata jita-jitar da ke cewa jirginta kirar C-130 da ya sauka ba tare da shiri ba a Bobo-Dioulasso,...

Duniya Za Ta Fuskanci Ƙalubale, Idan Najeriya Ta Wargaje– Inji Sanata Kashim Shettima

Mataimakin Shugaban Ƙasa a Najeriya, Kashim Shettima ya ce gwamnatin Tinubu ba za ta taɓa bari Najeriya ta ruguje a hannunta ba, komai rintsi.   Kamar yadda...

Most Popular