HomeSashen HausaƊan Wasan Ƙwallon Ƙafa Na Togo, Samuel Asamoah, Ya Karya Wuya A...

Ɗan Wasan Ƙwallon Ƙafa Na Togo, Samuel Asamoah, Ya Karya Wuya A Wani Wasa A Ƙasar China

-

Dan wasan tsakiyar ƙasar Togo, Samuel Asamoah, ya karye a wuya bayan karo da allon talla na gefen fili yayin wasa a kasar Sin, lamarin da kungiyar ƙwallon ƙafar da ya ke taka leda ta ce da wuya idan bai samu ciwon laka ba.

 

Asamoah, mai shekaru 31, wanda ke buga kwallo a kungiyar ƙwallon ƙafa ta Guangxi Pingguo na rukuni na biyu a kasar, ya bugu da kai cikin allon talla na LED bayan wani dan wasan abokan hamayya ya tura shi yayin wasan cikin gida da aka buga a ranar Lahadi.

 

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Litinin, kulob din Guangxi Pingguo ya bayyana cewa dan wasan yana cikin hadarin samun nakasar kafa (high-level paraplegia) bayan an gano yana da karaya da dama a wuya tare da raunin jijiyoyi masu tsanani.

 

An bayyana cewa an yi wa Asamoah tiyata kuma yana cikin halin da ya daidaita, yayin da kulob din ya ce za a ci gaba da sanar da jama’a ci gaban murmurewarsa bayan ƙarin gwaje-gwaje.

 

A yayin wasan, dan wasan tsakiyar Chongqing Tonglianglong, Zhang Zhixiong, ya karɓi katin gargadi saboda tura Asamoah cikin allon talla.

 

Asamoah ya shafe yawancin aikinsa a ƙasar Belgium kafin ya koma China a shekarar 2024, kuma yana da wasanni shida da ya wakilci ƙasar Togo a matakin kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano Wani barawon mota ya kutsa cikin Gidan Gwamnatin Kano da sanyin safiyar Litinin ya kuma...

‎Yansanda Sun Kama Masu Aikata Laifuka Daban-daban, Sun Ceto Mutane 47 da Aka Yi Garkuwa da Su a Jihar Katsina

Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Katsina ta bayyana cewa ta samu nasarori masu yawa a yakin da take yaki da laifuka, ciki har da kama mutanen...

Most Popular