HomeSashen HausaAn Rufe Jama'ar UMYUK Katsina Sai Baba Ta Gani

An Rufe Jama’ar UMYUK Katsina Sai Baba Ta Gani

-

An Rufe Jama’ar UMYUK Katsina Sai Baba Ta Gani

 

Kungiyoyin Malamai da ma’aikatan Jami’ar Ummaru Musa Yar’adua (UMYU) a Katsina sun tsunduma yajin aiki “sai baba ta gani” a ranar Litinin, 3 ga watan Nuwamba 2025.

 

Rahotanni sun bayyana cewa, yajin aikin ya shafi dukkan Malamai da ma’aikatan jami’ar, sakamakon wasu matsalolin da suke zargin gwamnati ta yi biris da su. Daga cikin korafe-korafen da suka gabatar sun hada da; Rashin ingantaccen jin daɗin ma’aikatan jami’ar, Matsalar kwace ikon gudanar da shafin (portal) na makaranta.

 

Sauran sun hada da Karancin kuɗaɗen gudanarwa, da kuma batun walwalar Ɗalibai.

 

Sai dai a nata ɓangaren, Gwamnatin Jihar Katsina ta yi watsi da korafe-korafen kungiyar, tare da jaddada cewa, tana ci gaba da ƙoƙarin magance dukkan matsalolin da suka shafi jami’ar da cigaban ilimi a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano Wani barawon mota ya kutsa cikin Gidan Gwamnatin Kano da sanyin safiyar Litinin ya kuma...

‎Yansanda Sun Kama Masu Aikata Laifuka Daban-daban, Sun Ceto Mutane 47 da Aka Yi Garkuwa da Su a Jihar Katsina

Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Katsina ta bayyana cewa ta samu nasarori masu yawa a yakin da take yaki da laifuka, ciki har da kama mutanen...

Most Popular