HomeSashen HausaTinubu Ya Ƙara Jaddda Umarnin Janye ’Yansanda Daga Gadin Manyan Mutane

Tinubu Ya Ƙara Jaddda Umarnin Janye ’Yansanda Daga Gadin Manyan Mutane

-

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ce ba za a sassauta umarnin janye ’yansanda daga gadin manyan jami’ai ba, yana mai gargadin dukkan ministoci su bi umarnin nan take.

 

Bayanin hakan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga ya fitar a yau Laraba.

 

A yayin taron majalisar zartarwa ta kasa, da aka gudanar a Abuja, Tinubu ya umarci mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Malam Nuhu Ribadu, Ministan Harkokin ’Yansanda Ibrahim Gaidam, da IG Kayode Egbetokun su tabbatar da an aiwatar da matakin.

 

Ya ce aikin ’yansanda shi ne kare al’umma, kuma za a maye gurbin su da jami’an Civil Defence wajen gadin manyan mutane.

 

Shugaban kasar ya ce sake tura ’yansanda aiki a fagen yaki da ’yan bindiga, garkuwa da mutane da ta’addanci zai inganta tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe...

Most Popular