HomeLabaraiTinubu Ya Ƙara Jaddda Umarnin Janye ’Yansanda Daga Gadin Manyan Mutane

Tinubu Ya Ƙara Jaddda Umarnin Janye ’Yansanda Daga Gadin Manyan Mutane

-

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ce ba za a sassauta umarnin janye ’yansanda daga gadin manyan jami’ai ba, yana mai gargadin dukkan ministoci su bi umarnin nan take.

 

Bayanin hakan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga ya fitar a yau Laraba.

 

A yayin taron majalisar zartarwa ta kasa, da aka gudanar a Abuja, Tinubu ya umarci mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Malam Nuhu Ribadu, Ministan Harkokin ’Yansanda Ibrahim Gaidam, da IG Kayode Egbetokun su tabbatar da an aiwatar da matakin.

 

Ya ce aikin ’yansanda shi ne kare al’umma, kuma za a maye gurbin su da jami’an Civil Defence wajen gadin manyan mutane.

 

Shugaban kasar ya ce sake tura ’yansanda aiki a fagen yaki da ’yan bindiga, garkuwa da mutane da ta’addanci zai inganta tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

ADC Ta Zargi Tinubu Da Raba Kan ‘Yan Adawa Ta Hanyar NDC

Jam’iyyar ADC ta yi zargin cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da jam’iyyar APC na da hannu wajen ƙirƙirar sabuwar jam’iyyar NDC domin raunata haɗin...

Vinicius Jr Accused of Reporting Teammates to Madrid Chiefs

Vinicius Jr Accused of Reporting Teammates’ Issues to Real Madrid Chiefs. Reports from several European media outlets claim that Vinícius Júnior is being accused of informing...

Most Popular