HomeSashen Hausa'Yansanda Sun Cafke Mai Gadi Da Abokinsa Kan Zargin Halaka Tsohuwar Mai...

‘Yansanda Sun Cafke Mai Gadi Da Abokinsa Kan Zargin Halaka Tsohuwar Mai Shari A Jihar Delta

-

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Delta ta tabbatar da kama mutum biyu da ake zargi da hannu a kisan gillar da aka yi wa tsohuwar alkaliyar Babban Kotun jihar, Mai Sharia Ifeoma Okogwu (Rtd.), wadda aka tsinci gawarta a falonta, hannayen ta ƙafafu da bakin a daure cikin yanayi mai tayar da hankali.

‎Mai magana da yawun rundunar, DSP Bright Edafe, ya bayyana cewa jami’an sashen binciken kisan kai na CID sun cafke wanda ake zargi, Godwin Mngumi, wanda shi ne mai gadi a gidan marigayiyar. An kama shi ne a jihar Anambra, kuma an same shi da wayar marigayiyar, alamar da ta ƙara tabbatar da zargin da ake masa.

‎A cewar Edafe, Mngumi ya amsa laifi, inda ya bayyana cewa shi ne ya shirya kai farmakin, tare da gayyatar wasu abokansa domin su taimaka wajen aikata wannan ta’asa.

‎“Ya amsa cewa ya gayyaci abokinsa Nnaji Obalum da wani mutum na uku da ya tsere. Sun kutsa cikin gidan ne suka yi kisan tare,” in ji Edafe cikin sanarwar.


‎Binciken ya kai ga kama Nnaji Obalum, yayin da ake cigaba da neman mutum na ukun da ya gudu domin fuskantar shari’a.

‎Tun farko dai, an gano gawar tsohuwar tsohuwar Mai Shari’arne a ranar 6 ga watan Disamba a gidanta da ke Asaba. Inda rahotanni suka tabbatar da cewa an sami alamun turjiya da cin zarafi a wajen, abin da ya tayar da hankalin mazauna unguwar da al’ummar jihar baki ɗaya.

‎Rundunar ’yan sandan ta ce tana ci gaba da zurfafa bincike don tabbatar da cewa duk masu hannu a wannan aika-aika sun fuskanci hukunci yadda doka ta tanada.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina Police Received 29 New ASPs From The Nigeria Police Academy, Wudil

The Katsina State Police Command has received 29 newly posted Assistant Superintendents of Police (ASPs) from the Nigeria Police Academy, Wudil. Welcoming the officers, the...

Yawancin Fulanin Da Suke Ta’addanci Ba Su Da Addini, Ba Su San Allah Ba– Nasir El Rufa’i ‎

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufa’i, ya bayyana cewa yawancin mutanen Fulani da ake zargi da aikata ta'addanci da kashe kashe a sassa daban...

Most Popular