Friday, June 26, 2026
HomeLabarai‎APC Ta Shirya Karɓar Gwamnan Plateau a Wata Mai Zuwa

‎APC Ta Shirya Karɓar Gwamnan Plateau a Wata Mai Zuwa

‎Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta tabbatar da shirinta na karɓar Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Mutfwang, a wata mai zuwa, lamarin da ya fara jawo muhawara a fagen siyasar jihar da ma ƙasa baki ɗaya.

‎Shugabannin jam’iyyar sun bayyana cewa ana dab da kammala shirye-shiryen maraba da gwamnan, inda suka ce hakan wani mataki ne na ƙarfafa APC a Plateau tare da faɗaɗa haɗin kai a tsakanin manyan ‘yan siyasa gabanin zaɓukan da ke tafe.

‎Wata majiya a cikin jam’iyyar ta ce zuwan Gwamna Mutfwang APC na iya sauya taswirar siyasar Plateau, musamman ganin irin tasirin da yake da shi a cikin al’umma da kuma muhimman ƙudurorin ci gaba da gwamnatinsa ke aiwatarwa.

‎Sai dai har zuwa yanzu, Gwamna Mutfwang bai fitar da cikakken bayani ba akan wannan shiri, duk da cewa magoya baya da masu sharhi na ci gaba da dakon lamarin.

‎Masana siyasa na ganin wannan mataki, idan ya tabbata, zai zama babban lamari a siyasar Arewa ta Tsakiya, tare da yiwuwar yin tasiri ga daidaiton jam’iyyun siyasa a nan gaba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments