HomeSashen HausaMun Ji Dadin Haɗin Kan Da Najeriya Ta Ba Mu Wajen Kai...

Mun Ji Dadin Haɗin Kan Da Najeriya Ta Ba Mu Wajen Kai Farmaki A Yankunan Ƙasar– Amurka

-

Sakataren yaƙi na Amurka ya yaba wa gwamnatin Najeriya bisa goyon bayan da ta bayar bayan kai hare-haren bama-bamai kan wuraren da ‘yan ta’adda suke.

 

Sakataren yaƙi na Amurka, Pete Hegseth, ya yaba wa hwamnatin Najeriya saboda haɗin kai da goyon bayan da ta bayar bayan wani harin jirgin yaki da Amurka ta jagoranta, wanda aka kai kan wadanda ake zargin ‘yan ta’adda ne ajihar Sokoto.

 

Jaridar Daily Nigerian ta rawaito cewa harin na sama, wanda ya faru a ranar Alhamis, ya auku ne a wani wuri da ke kaauyen Jabo a jihar Sokoto.

 

Wannan hari yana cikin wani babban shiri na yaƙi da ta’addanci da gwamnatin Amurka ke aiwatarwa tare da haɗin gwiwar hukumomin Najeriya.

 

Sai dai, mazauna garin Jabo sun ce babu wanda ya rasa ransa a harin.

 

A cewar mazauna kauyen, daga baya mutane da dama sun taru a wurin da fashewar ta faru, inda suka tabbatar cewa ba a rasa rai ko guda ba.

 

Da yake mayar da martani game da harin, Mista Hegseth, ta cikin wani sakon da ya wallafa a kafar sada zumunta, ya ce wannan mataki ya nuna cewa ma’aikatar yaƙi ta Amurka na da shiri tsaf wajen mayar da martani cikin gaggawa kan barazanar ta’addanci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe...

Most Popular