HomeLabaraiMun Ji Dadin Haɗin Kan Da Najeriya Ta Ba Mu Wajen Kai...

Mun Ji Dadin Haɗin Kan Da Najeriya Ta Ba Mu Wajen Kai Farmaki A Yankunan Ƙasar– Amurka

-

Sakataren yaƙi na Amurka ya yaba wa gwamnatin Najeriya bisa goyon bayan da ta bayar bayan kai hare-haren bama-bamai kan wuraren da ‘yan ta’adda suke.

 

Sakataren yaƙi na Amurka, Pete Hegseth, ya yaba wa hwamnatin Najeriya saboda haɗin kai da goyon bayan da ta bayar bayan wani harin jirgin yaki da Amurka ta jagoranta, wanda aka kai kan wadanda ake zargin ‘yan ta’adda ne ajihar Sokoto.

 

Jaridar Daily Nigerian ta rawaito cewa harin na sama, wanda ya faru a ranar Alhamis, ya auku ne a wani wuri da ke kaauyen Jabo a jihar Sokoto.

 

Wannan hari yana cikin wani babban shiri na yaƙi da ta’addanci da gwamnatin Amurka ke aiwatarwa tare da haɗin gwiwar hukumomin Najeriya.

 

Sai dai, mazauna garin Jabo sun ce babu wanda ya rasa ransa a harin.

 

A cewar mazauna kauyen, daga baya mutane da dama sun taru a wurin da fashewar ta faru, inda suka tabbatar cewa ba a rasa rai ko guda ba.

 

Da yake mayar da martani game da harin, Mista Hegseth, ta cikin wani sakon da ya wallafa a kafar sada zumunta, ya ce wannan mataki ya nuna cewa ma’aikatar yaƙi ta Amurka na da shiri tsaf wajen mayar da martani cikin gaggawa kan barazanar ta’addanci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina Police Foil Kidnap Attempt, Rescue 18-Year-Old Girl in Danmusa LG

The Katsina State Police Command has foiled a kidnapping attempt and rescued an 18-year-old girl in Danmusa Local Government Area following a swift response by...

Harin Sojin Sama a Zamfara Ya Hallaka Sama da Mutane 100

A cikin wata sanarwa da rundunar Operation Fansan Yamma ta fitar, ta ce an kai harin ne bayan samun sahihan bayanan sirri da suka nuna...

Most Popular