HomeSashen Hausa‎Majalisar Wakilai Ta Umarci A Yi Gyare-gyare a Kundin Sabbin Dokokin Haraji...

‎Majalisar Wakilai Ta Umarci A Yi Gyare-gyare a Kundin Sabbin Dokokin Haraji Bayan Samun Kura-kurai

-

Majalisar Wakilai ta bayar da umarnin sake duba sabbin dokokin gyaran haraji da aka amince da su kwanan nan, biyo bayan zargin bambance-bambance tsakanin dokokin da majalisar ƙasa ta amince da su da kuma waɗanda aka wallafa bayan shugaban ƙasa ya sanya hannu.

‎Kakakin Majalisar, Akin Rotimi, ya ce matakin ya zama dole domin kare mutuncin majalisa, tabbatar da bin ƙa’idoji, da dawo da amincewar jama’a ga tsarin yin dokoki.

‎Ya bayyana cewa duk wani bambanci tsakanin kudurin doka da aka amince da shi da waɗanda aka wallafa na tauye dimokuraɗiyya da manufar dokoki.

‎Majalisar ta jaddada cewa dokokin haraji, saboda tasirinsu ga tattalin arziƙi, dole ne su kasance a bayyane, daidai, kuma bisa tsarin kundin mulki.

‎Ta kuma tabbatar da cewa za ta yi aiki da hukumomin zartarwa domin gyara matsalar tare da hana sake faruwarta, tana mai jaddada goyon baya ga gyare-gyaren da ke ƙarfafa tattalin arziƙi matuƙar an bi ka’idojin doka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Afenifere Ta Goyi Bayan Harin Da Amurka Ta Kai a Sokoto

Kungiyar Afenifere, wadda ke wakiltar al’ummar Yarbawa a fannin siyasa da zamantakewa, ta bayyana goyon bayanta ga hare-haren jiragen yakin Amurka da aka kai kan...

Harin Da Amurka Ta Kai ‘Yan ta’adda Ne Kaɗai Ya Shafa– Inji Gwamnatin Sokoto

Gwamnatin Jihar Sokoto ta tabbatar da cewa harin sama na haɗin gwiwar sojojin Najeriya da Amurka ya kai hari kan sansanonin ’yan ta’adda a ƙaramar...

Most Popular