Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Ƙasa da Ƙasa (IFJ) ta ce jimillar ’yan jarida 128 aka kashe a fadin duniya a shekarar 2025, kuma fiye da rabinsu a yankin Gabas ta Tsakiya suke.
Sakataren Janar na IFJ, Anthony Bellanger, ya shaida wa AFP cewa wannan adadi mai muni, wanda ya karu daga na shekarar 2024, “ba wai kididdiga ba ce kawai, illa wani gargaɗin duniya ga abokan aikinmu.”
Ƙungiyar ta nuna damuwa musamman kan halin da ake ciki a yankunan Falasdinu, inda ta ce ta kiyaye mutuwar ’yan jarida 56 a shekarar 2025 yayin da yaƙin Isra’ila da Hamas ya ci gaba a Gaza.
