HomeSashen Hausa‎'Yansanda A Jihar Zamfara, Sun Yi Nasarar Dakile Wani Hari Da ‘Yanbindiga...

‎’Yansanda A Jihar Zamfara, Sun Yi Nasarar Dakile Wani Hari Da ‘Yanbindiga Suka Kai Jihar

-

Rundunar ‘Yansanda a jihar Zamfara, a karkashin sashin yaki da masu satar mutane, sun yi nasarar dakile wani hari da ‘yan fashin daji suka kai da ceto mata da yara kanana biyar a kan hanyar Gusau zuwa Dansadau.

‎Kakakin rundunar ’yan sandan, DSP Yazid Abubakar, ya ce jami’an na sintiri ne lokacin da suka ci karo da ‘yan fashin sun tare motoci, inda aka yi musayar wuta da ta tilasta wa bata-garin tserewa cikin daji da raunukan harbi tare da barin mutanen da suka yi yunkurin sacewa.

‎Wadanda aka ceto suna tafiya ne daga Wanke zuwa Gusau kafin maharan su yi awon gaba da su.

‎Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Ibrahim Balarabe Maikaba, ya tabbatar da cewa an duba lafiyar wadanda aka ceton kuma tuni aka hada su da iyalansu, yayin da ya nanata kudurin rundunar na kare rayuka da dukiyoyin al’umma tare da yin kira ga jama’a da su ci gaba da ba da bayanan sirri ga hukumomi akan lokaci

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe...

Most Popular