HomeLabarai‎'Yansanda A Jihar Zamfara, Sun Yi Nasarar Dakile Wani Hari Da ‘Yanbindiga...

‎’Yansanda A Jihar Zamfara, Sun Yi Nasarar Dakile Wani Hari Da ‘Yanbindiga Suka Kai Jihar

-

Rundunar ‘Yansanda a jihar Zamfara, a karkashin sashin yaki da masu satar mutane, sun yi nasarar dakile wani hari da ‘yan fashin daji suka kai da ceto mata da yara kanana biyar a kan hanyar Gusau zuwa Dansadau.

‎Kakakin rundunar ’yan sandan, DSP Yazid Abubakar, ya ce jami’an na sintiri ne lokacin da suka ci karo da ‘yan fashin sun tare motoci, inda aka yi musayar wuta da ta tilasta wa bata-garin tserewa cikin daji da raunukan harbi tare da barin mutanen da suka yi yunkurin sacewa.

‎Wadanda aka ceto suna tafiya ne daga Wanke zuwa Gusau kafin maharan su yi awon gaba da su.

‎Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Ibrahim Balarabe Maikaba, ya tabbatar da cewa an duba lafiyar wadanda aka ceton kuma tuni aka hada su da iyalansu, yayin da ya nanata kudurin rundunar na kare rayuka da dukiyoyin al’umma tare da yin kira ga jama’a da su ci gaba da ba da bayanan sirri ga hukumomi akan lokaci

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina Police Arrest Suspected Kidnapper, Bandit Informant in Matazu

The Katsina State Police Command has arrested a 45-year-old man, identified as Surajo Isyaku, over alleged involvement in kidnapping, cattle rustling and providing information to...

Dangote Refinery Reduces Aviation Fuel Price by N100 Per Litre

Dangote Refinery has announced a reduction in the price of Jet A1 aviation fuel from N1,750 to N1,650 per litre, in a move aimed at...

Most Popular