HomeLabaraiTrump Ya Janye Jakadan Amurka daga Nijeriya

Trump Ya Janye Jakadan Amurka daga Nijeriya

-

Shugaban ƙasar Amurka, Donald Trump, ya bayar da umarnin janye jakadan ƙasar daga Najeriya, Richard Mills, a wani bangare na sauyin tsarin diflomasiyya da ya shafi sama da ƙasashe 20 a duniya.

Najeriya na cikin ƙasashe 15 na Afirka da abin ya shafa, tare da wasu ƙasashe irinsu Masar, Senegal, Rwanda, Uganda, Nijar da Kamaru. An kuma aiwatar da matakin a wasu ƙasashen Asiya, Turai da Amurka ta Tsakiya da Kudu.

Rahotanni sun nuna cewa dukkan jakadun da aka janye an nada su ne a zamanin tsohon shugaban Amurka, Joe Biden, kuma an sanar da su cewa wa’adin aikinsu zai ƙare a watan Janairu mai zuwa.

Richard Mills ya fara aiki a Najeriya a Mayu na bara, kuma janyewarsa na zuwa ne a daidai lokacin da ake fuskantar ɗan tangarda a dangantakar diflomasiyya tsakanin Najeriya da Amurka, musamman kan batutuwan biza da tsaro, duk da ci gaba da tattaunawa tsakanin ɓangarorin biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Brazil Doesn’t Necessarily Have to Win the World Cup –Vinícius

Renowned Brazilian footballer Vinícius Júnior stated that his country does not necessarily have to be among the teams that win the 2026 FIFA World Cup. He...

OMOS Continues to Fly Nigeria’s Flag High in WWE

Renowned wrestling star Omos continues to represent Nigeria on the global stage of WWE, where he stands among the tallest athletes in the world. Omos has...

Most Popular