Jagororin jam’iyyun hamayya na Najeriya a ƙarƙashin inuwar ƙungiyar hadaƙa ta Nigeria National Coalition Group (NNCG) na neman rajistar All Democratic Alliance (ADA) domin ta zama sabuwar jam’iyyar da za su yi amfani da ita domin fafatawa da jam’iyyar APC a zaɓe mai zuwa.
Nigerian Post ta samu cewa, tuni NNCG ta miƙa takardar neman rajistar jam’iyya ga Hukumar INEC a hukumance, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
Wasiƙar wadda suka aika zuwa ga shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu a ranar 19 ga watan Yuni, shugaban ADA na ƙasa Cif Akin Ricketts da sakataren riƙo Abdullahi Musa Elayo ne suka sanya mata hannu, sannan INEC ta karɓa tare a ranar 20 ga Yunin.
A wasiƙar, sun rubuta cewa, “muna neman INEC ta amince da buƙatarmu ta yi wa ƙungiyarmu ta All Democratic Alliance ta zama jam’iyyar siyasa.”
Taken jam’iyyar dai shi ne ‘Adalci ga kowa’ sannan masara ce tambarinta.
Daga cikin na gaba-gaba wajen yunƙurin samar da haɗaka da za ta fuskanci jam’iyyar APC mai mulki akwai tsohon shugaban Najeriya Atiku Abubakar da tsohon gwamnan jihar Ribas Rotimi Amaechi da tsohon gwamnan Kaduna Nasir El-Rufai da tsohon shugaban majalisar dattawar ƙasar, Sanata David Mark da Umar Arɗo da sauransu.