HomeSashen HausaAn ƙaddamar da sabbin jami'ai da za su rinƙa ba 'Yansanda bayanai...

An ƙaddamar da sabbin jami’ai da za su rinƙa ba ‘Yansanda bayanai a Katsina

-

Babban uba ga PCRC Alhaji Sabo Musa, ya jagoranci ƙaddamar da sabbin jami’ai da za su rinƙa ba ‘Yandanda bayanai a ƙananan hukumomi 8, da suka haɗa da Dandume, ƙaramar hukumar Katsina, Dutsinma, da sauran su.

Majiyar ta samu cewa, an kaddamar da su ne domin bada bayanai a kowacce Unguwa a jihar, da kuma kashe duk wasu fitintinu a cikin unguwanni, idan abin kuma ya fi karfinsu su kai rahota ga manyan jami’an tsaro.

Lokacin da ake ƙaddamar da su, masu ruwa da tsaki na ɓangaren tsaro a jihar Katsina sun ziyarci taron, domin haɗa kai da duk wani sashe na jami’an tsaro a jihar.

A wani rahoto da Nigerian Post ta samu, lokacin da ake ƙaddamar da shuwagabannin jami’an a jihar, Alhaji Sabo Musa, shi ne a ƙaddamar da su a ranar Lahadi da ta gaba a birnin Katsina.

An kuma ja kunnen su da su kasance ma su gaskiya da amana ba tare da sun ci amanar yankunan su ba ko kuma karya dokar da ta shafi ƙasa, an ce ma su, ya zama wajibi su bi doka da oda kar su kasance sun tauye haƙƙin wasu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe...

Most Popular