HomeSashen HausaRashin samun mulki ne ya sa masu haɗaka kumfar baki -inji Dikko...

Rashin samun mulki ne ya sa masu haɗaka kumfar baki -inji Dikko Radda

-

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa, ya ce ba komai ne ya sa masu haɗaka suke kumfar baki ba shi ne, saboda rashin samun muƙami wanda har suka ƙirƙiro wai wata haɗaka da suke ganin kamar al’umma za su yarda da su.

Raɗɗa ya bayyana haka a lokacin da ake tattaunawa da shi a shirin Sunrise Daily na Channels TV, ranar Talata, inda ya ke cewa, lokaci ya wuce da za a ci gaba da yaudarar ‘yan Najeriya domin kar suke kallon kowa.

A cewar sa, waɗanda suke ƙoƙarin yin haɗakar su ne sukai mulki jiya, kuma suna sane da tarihin kowa, kuma sun san duk abin da suka aikata mai kyau ko marar kyau a lokacin da suke cikin gwamnatin baya.

Haka kuma, Malam Dikko Umaru Raɗɗa, ya caccaki haɗakar tare da ɗora ayar tambaya sahihancin manufarta da kuma gaskiyar dalilin kafuwarta, inda ya jaddada cewa, yanzu ya rage ma ‘yan Najeriya sai su yi alƙalanci da kan su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe...

Most Popular