Matasa a lungu da saƙo na sassan ƙasar Najeriya, suna ci gaba da gangamin bikin tunawa da ranar Matasa ta Duniya, inda su ke ci gaba da bayyana ci gaban da Matasa suka samu da kuma akasin haka.
Nigerian Post ta bibiyi cewa, Majalisar Ɗinkin Duniya ta ƙirƙiro ranar Matasa ta Duniya a shekarar 1999, inda aka fara gudanar da bikin a shekarar 12 ga watan Augustan na shekarar 2000.
Tunda farko, Majalisar Ɗinkin Duniya dai, ta ware ranar 12 ga watan Augustan na kowacce shekara a matsayin ranar Matasa.
Masu fashin baƙi da al’amuran yau da kullum, suna yawan cewa, Matasa su ne ƙashin bayan al’umma, idan Matasa suka gyara makomar su to al’umma za ta gyaru kashi 88 cikin 100.