HomeSashen HausaKatsina United Ta Doke Kano Pillars Da 1-0 A Muhammadu Dikko Stadium

Katsina United Ta Doke Kano Pillars Da 1-0 A Muhammadu Dikko Stadium

-

Katsina United Ta Doke Kano Pillars Da 1-0 A Muhammadu Dikko Stadium

Katsina United ta samu nasarar doke abokiyar hamayyarta, Kano Pillars, da ci 1–0 a wasan gasar Firimiya lig na Kwararru ta Najeriya da aka fafata a filin wasa na Muhammadu Dikko, cikin garin Katsina.

An buga wasan ne cikin tsananin ƙwarewa da hazaƙa inda bangarorin biyu suka nuna gogwarsu su a fagen kwallon kafa, sai dai mintuna na ƙarshen wasa ne Katsina United ta samu damar zura kwallo ta hannun ɗan wasanta, Azeez Falalu, wanda hakan ya bai wa masu masaukin baƙi nasara.

Magoya baya daga sassa daban-daban na jihar Katsina da Kano ne dai, suka halarci wasan, inda suka nuna farin cikinsu ko da yake sakamakon bai yi ma wasu dadi ba.

Hukumar gudanar da wasa ta tabbatar da cewa wannan nasara ta Katsina United zai ƙara mata maki a teburin gasar, yayin da Kano Pillars za ta sake ƙoƙari a wasanta na gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano Wani barawon mota ya kutsa cikin Gidan Gwamnatin Kano da sanyin safiyar Litinin ya kuma...

‎Yansanda Sun Kama Masu Aikata Laifuka Daban-daban, Sun Ceto Mutane 47 da Aka Yi Garkuwa da Su a Jihar Katsina

Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Katsina ta bayyana cewa ta samu nasarori masu yawa a yakin da take yaki da laifuka, ciki har da kama mutanen...

Most Popular