HomeSashen HausaKatsina United Ta Doke Kano Pillars Da 1-0 A Muhammadu Dikko Stadium

Katsina United Ta Doke Kano Pillars Da 1-0 A Muhammadu Dikko Stadium

-

Katsina United Ta Doke Kano Pillars Da 1-0 A Muhammadu Dikko Stadium

Katsina United ta samu nasarar doke abokiyar hamayyarta, Kano Pillars, da ci 1–0 a wasan gasar Firimiya lig na Kwararru ta Najeriya da aka fafata a filin wasa na Muhammadu Dikko, cikin garin Katsina.

An buga wasan ne cikin tsananin ƙwarewa da hazaƙa inda bangarorin biyu suka nuna gogwarsu su a fagen kwallon kafa, sai dai mintuna na ƙarshen wasa ne Katsina United ta samu damar zura kwallo ta hannun ɗan wasanta, Azeez Falalu, wanda hakan ya bai wa masu masaukin baƙi nasara.

Magoya baya daga sassa daban-daban na jihar Katsina da Kano ne dai, suka halarci wasan, inda suka nuna farin cikinsu ko da yake sakamakon bai yi ma wasu dadi ba.

Hukumar gudanar da wasa ta tabbatar da cewa wannan nasara ta Katsina United zai ƙara mata maki a teburin gasar, yayin da Kano Pillars za ta sake ƙoƙari a wasanta na gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎Kim Jong Un Ya Zaɓi Ƴarsa Mai Shekara 13 a Matsayin Wadda Za Ta Gaje Shi ‎

Rahotanni daga National Intelligence Service (NIS) sun bayyana cewa shugaban Koriya ta Arewa, Kim Jong Un, ya zaɓi ƴarsa mai shekara 13, Kim Ju Ae,...

‎’Yan Najeriya Biyu Sun Mutu a Yaƙin Ukraine

Rahotanni sun bayyana cewa wasu ƴan Najeriya biyu – Hamzat Kazeem Kolawale da Mbah Stephen Udoka – sun rasu a ƙasar Ukraine yayin da suke...

Most Popular