HomeSashen HausaZa a Dinga Koyar Da Yaren Chana A Makaratun Sakandare Na Najeriya-...

Za a Dinga Koyar Da Yaren Chana A Makaratun Sakandare Na Najeriya- Gwamnatin Taraiya

-

Za a Dinga Koyar Da Yaren Chana A Makaratun Sakandare Na Najeriya- Gwamnatin Taraiya

Gwamnatin Tarayya ta sanar da saka harshen Chana (Mandarin) a cikin kundin karatun makarantun sakandare a Najeriya.

Sakataren Ilimi na Abuja, Dakta Danlami Hayyo ne ya bayyana hakan a Abuja yayin kaddamar da “Chinese Corner” na 14, inda ya ce wannan mataki na nuna muhimmancin harshen Mandarin a kasuwanci, ilimi, al’adu da diflomasiyya.

Ya ce koyar da ɗalibai harshen zai ba su damar gogayya a duniya tare da samun damar ilimi da kasuwanci.

A cewarsa, wannan shiri wani bangare ne na ƙoƙarin gwamnati wajen shirya matasa domin zama masu iya yin gogayya a fagen duniya.

Ana ganin matakin zai kara zurfafa dangantakar Najeriya da ƙasar China a fannoni da dama, musamman ilimi da musayar al’adu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Hukumar NSCDC A Katsina Ta Yi Sabon Shugaba

Hukumar Tsaro ta NSCDC reshen Jihar Katsina ta samu sabon kwamanda bayan sauyin shugabanci da ya gudana a ranar Litinin, 22 ga watan Satumba, 2025.   A...

Gwamnatin Jihar Katsina Ta Horas Da Malamai 250 Da Faransifal 50, Don Inganta Ilmin Jihar

Ma’aikatar Ilimi a Matakin Farko da na Sakandire a jihar Katsina, haɗin gwiwa da Majalisar Turai (British Council), ta ƙaddamar da wani muhimmin shirin horaswa...

Most Popular