HomeSashen HausaZa a Dinga Koyar Da Yaren Chana A Makaratun Sakandare Na Najeriya-...

Za a Dinga Koyar Da Yaren Chana A Makaratun Sakandare Na Najeriya- Gwamnatin Taraiya

-

Za a Dinga Koyar Da Yaren Chana A Makaratun Sakandare Na Najeriya- Gwamnatin Taraiya

Gwamnatin Tarayya ta sanar da saka harshen Chana (Mandarin) a cikin kundin karatun makarantun sakandare a Najeriya.

Sakataren Ilimi na Abuja, Dakta Danlami Hayyo ne ya bayyana hakan a Abuja yayin kaddamar da “Chinese Corner” na 14, inda ya ce wannan mataki na nuna muhimmancin harshen Mandarin a kasuwanci, ilimi, al’adu da diflomasiyya.

Ya ce koyar da ɗalibai harshen zai ba su damar gogayya a duniya tare da samun damar ilimi da kasuwanci.

A cewarsa, wannan shiri wani bangare ne na ƙoƙarin gwamnati wajen shirya matasa domin zama masu iya yin gogayya a fagen duniya.

Ana ganin matakin zai kara zurfafa dangantakar Najeriya da ƙasar China a fannoni da dama, musamman ilimi da musayar al’adu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

SAKON ƘARSHEN SHEKARA NA KATSINA TIMES: Mun Fuskanci Barazana Da Kalubale A Shekarar 2025– Inji Malam Muhammad Danjuma Katsina

Tunda farko, ya yi godiya ga Allah Maɗaukakin Sarki, tare da salati da aminci ga Manzon Rahama, Annabi Muhammad (SAW), iyalansa (AS) da sahabbansa (RA),...

Obi Na Shirin Shiga ADC Yayin Da Jam’iyyar Za Ta Yi Babban Taron Ta Na Ƙasa a 2026

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na Labour Party (LP), Peter Obi, na dab da shiga jam’iyyar ADC, gabanin babban zaɓen shekarar 2027. Wata majiya a jam’iyyar...

Most Popular