HomeLabaraiZa a Dinga Koyar Da Yaren Chana A Makaratun Sakandare Na Najeriya-...

Za a Dinga Koyar Da Yaren Chana A Makaratun Sakandare Na Najeriya- Gwamnatin Taraiya

-

Za a Dinga Koyar Da Yaren Chana A Makaratun Sakandare Na Najeriya- Gwamnatin Taraiya

Gwamnatin Tarayya ta sanar da saka harshen Chana (Mandarin) a cikin kundin karatun makarantun sakandare a Najeriya.

Sakataren Ilimi na Abuja, Dakta Danlami Hayyo ne ya bayyana hakan a Abuja yayin kaddamar da “Chinese Corner” na 14, inda ya ce wannan mataki na nuna muhimmancin harshen Mandarin a kasuwanci, ilimi, al’adu da diflomasiyya.

Ya ce koyar da ɗalibai harshen zai ba su damar gogayya a duniya tare da samun damar ilimi da kasuwanci.

A cewarsa, wannan shiri wani bangare ne na ƙoƙarin gwamnati wajen shirya matasa domin zama masu iya yin gogayya a fagen duniya.

Ana ganin matakin zai kara zurfafa dangantakar Najeriya da ƙasar China a fannoni da dama, musamman ilimi da musayar al’adu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina Police Foil Kidnap Attempt, Rescue 18-Year-Old Girl in Danmusa LG

The Katsina State Police Command has foiled a kidnapping attempt and rescued an 18-year-old girl in Danmusa Local Government Area following a swift response by...

Harin Sojin Sama a Zamfara Ya Hallaka Sama da Mutane 100

A cikin wata sanarwa da rundunar Operation Fansan Yamma ta fitar, ta ce an kai harin ne bayan samun sahihan bayanan sirri da suka nuna...

Most Popular