HomeSashen HausaMa'aikatar Shari'a Ta Katsina Ta Naɗa Mace Ta Farko A Matsayin Babbar...

Ma’aikatar Shari’a Ta Katsina Ta Naɗa Mace Ta Farko A Matsayin Babbar Magatakarda

-

Ma’aikatar Shari’a ta jihar Katsina ta naɗa Basira Umar a matsayin mace ta farko da za ta rike mukamin Babbar Magatakarda ta Babbar Kotun Katsina tun bayan kafa jihar a 1987.

 

A rahoton Daily Nigerian, wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Musa Usman, Daraktan Hulda da Jama’a na Babbar Kotun jihar, ya fitar ga manema labarai a Katsina a ranar Asabar.

 

A cewarsa, wannan naɗin ya biyo bayan ritayar Malam Mustapha Hassan-Rumah daga aikin gwamnati.

 

Ya bayyana cewa Babban Magatakarda shi ne babban jami’in kula da dukiyar kotu, wanda ke da alhakin tsarawa da gudanar da kasafin kuɗi da sauran harkokin kuɗi.

 

“Haka kuma Babban Magatakarda shi ne shugaban gudanarwa na ma’aikatar shari’a, wanda ke jagorantar harkokin yau da kullum.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

SAKON ƘARSHEN SHEKARA NA KATSINA TIMES: Mun Fuskanci Barazana Da Kalubale A Shekarar 2025– Inji Malam Muhammad Danjuma Katsina

Tunda farko, ya yi godiya ga Allah Maɗaukakin Sarki, tare da salati da aminci ga Manzon Rahama, Annabi Muhammad (SAW), iyalansa (AS) da sahabbansa (RA),...

Obi Na Shirin Shiga ADC Yayin Da Jam’iyyar Za Ta Yi Babban Taron Ta Na Ƙasa a 2026

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na Labour Party (LP), Peter Obi, na dab da shiga jam’iyyar ADC, gabanin babban zaɓen shekarar 2027. Wata majiya a jam’iyyar...

Most Popular