HomeSashen Hausa'Yan Bindigar Da Suka Sace Mutane 3 A Tsakiyar Katsina Sun Nemi...

‘Yan Bindigar Da Suka Sace Mutane 3 A Tsakiyar Katsina Sun Nemi Miliyan 600 Kuɗin Fansa

-

Wasu ’yan bindiga da suka sace wasu ma’aurata da ’yarsu yayin wani hari da suka kai a unguwar Filin Canada da ke Sabuwar Unguwa a cikin birnin Katsina, sun tuntubi dangin wadanda aka sace suna neman kudin fansa har Naira miliyan 600.

Wata majiyar daga cikin dangin wadanda akayi garkuwar, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana hakan ga majiyarmu ta jaridar Daily Trust a jiya.

An sace Anas Ahmadu mai shekaru 33, matarsa Halimat, da ’yarsu Jidda, a safiyar ranar Talata.

Rahotannin dai sun bayyana cewa Wani dan sa-kai mai suna Abdullahi Muhammad mai shekaru 25, ya rasa ransa bayan da aka harbe shi yayin da yake kokarin ceto wadanda aka sace daga hannun masu garkuwar da suka tsere kafin zuwan jami’an tsaro.

Majiyar ta bayyana cewa lambar wayar Anas ce aka yi amfani da ita wajen kiran kawun matarsa, Malam Ibrahim, domin neman kudin fansa a jiya.

Sai dai an bayyana cewa sun shaida wa masu garkuwar cewa dangin ba za su iya biya kudin da ake bukata ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina Police Received 29 New ASPs From The Nigeria Police Academy, Wudil

The Katsina State Police Command has received 29 newly posted Assistant Superintendents of Police (ASPs) from the Nigeria Police Academy, Wudil. Welcoming the officers, the...

Yawancin Fulanin Da Suke Ta’addanci Ba Su Da Addini, Ba Su San Allah Ba– Nasir El Rufa’i ‎

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufa’i, ya bayyana cewa yawancin mutanen Fulani da ake zargi da aikata ta'addanci da kashe kashe a sassa daban...

Most Popular