HomeLabarai‎Ɗan Jihar Katsina Ya Sami Mukami Mai Girma a Hukumar NDLEA

‎Ɗan Jihar Katsina Ya Sami Mukami Mai Girma a Hukumar NDLEA

-

Wani ɗan asalin jihar Katsina, Ahmed Idris Zakari, ya sami ƙarin girma a Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA), inda aka naɗa shi zuwa mukamin Assistant Commander General of NDLEA, wani mukami dake daf da na ƙarshe a tsarin shugabancin hukumar.

Ahmed Idris Zakari, wanda ya fito daga ƙaramar hukumar Katsina, ya samu wannan matsayi ne sakamakon jajircewarsa, kwarewa da kuma gudummawar da ya bayar tsawon shekarun da ya shafe yana aiki a hukumar, musamman a fannin yaƙi da miyagun ƙwayoyi da kare lafiyar al’umma.

Masu ruwa da tsaki da dama sun bayyana wannan cigaba a matsayin abin alfahari ga jihar Katsina dama Arewa gaba ɗaya, inda suka yaba da yadda ƴayan jihar ke cigaba da samun manyan mukamai a hukumomin ƙasa.

An yi addu’ar Allah Ya sanya alheri a wannan ƙarin girma, Ya kuma ba shi ikon sauke nauyin da aka ɗora masa cikin adalci da gaskiya, tare da cigaba da bada gudummawa wajen yaƙi da miyagun ƙwayoyi a Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina Police Foil Kidnap Attempt, Rescue 18-Year-Old Girl in Danmusa LG

The Katsina State Police Command has foiled a kidnapping attempt and rescued an 18-year-old girl in Danmusa Local Government Area following a swift response by...

Harin Sojin Sama a Zamfara Ya Hallaka Sama da Mutane 100

A cikin wata sanarwa da rundunar Operation Fansan Yamma ta fitar, ta ce an kai harin ne bayan samun sahihan bayanan sirri da suka nuna...

Most Popular