HomeSashen Hausa‎Ɗan Jihar Katsina Ya Sami Mukami Mai Girma a Hukumar NDLEA

‎Ɗan Jihar Katsina Ya Sami Mukami Mai Girma a Hukumar NDLEA

-

Wani ɗan asalin jihar Katsina, Ahmed Idris Zakari, ya sami ƙarin girma a Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA), inda aka naɗa shi zuwa mukamin Assistant Commander General of NDLEA, wani mukami dake daf da na ƙarshe a tsarin shugabancin hukumar.

Ahmed Idris Zakari, wanda ya fito daga ƙaramar hukumar Katsina, ya samu wannan matsayi ne sakamakon jajircewarsa, kwarewa da kuma gudummawar da ya bayar tsawon shekarun da ya shafe yana aiki a hukumar, musamman a fannin yaƙi da miyagun ƙwayoyi da kare lafiyar al’umma.

Masu ruwa da tsaki da dama sun bayyana wannan cigaba a matsayin abin alfahari ga jihar Katsina dama Arewa gaba ɗaya, inda suka yaba da yadda ƴayan jihar ke cigaba da samun manyan mukamai a hukumomin ƙasa.

An yi addu’ar Allah Ya sanya alheri a wannan ƙarin girma, Ya kuma ba shi ikon sauke nauyin da aka ɗora masa cikin adalci da gaskiya, tare da cigaba da bada gudummawa wajen yaƙi da miyagun ƙwayoyi a Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina Police Received 29 New ASPs From The Nigeria Police Academy, Wudil

The Katsina State Police Command has received 29 newly posted Assistant Superintendents of Police (ASPs) from the Nigeria Police Academy, Wudil. Welcoming the officers, the...

Yawancin Fulanin Da Suke Ta’addanci Ba Su Da Addini, Ba Su San Allah Ba– Nasir El Rufa’i ‎

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufa’i, ya bayyana cewa yawancin mutanen Fulani da ake zargi da aikata ta'addanci da kashe kashe a sassa daban...

Most Popular