HomeSashen HausaBa Da Jimawa Ba Za Mu Kawo Ƙarshen Rikicin Masarautar Kano– Gwamnatin...

Ba Da Jimawa Ba Za Mu Kawo Ƙarshen Rikicin Masarautar Kano– Gwamnatin Kano

-

Gwamnatin jihar Kano ta ce nan ba jimawa ba za ta kawo karshen rikicin da ya daɗe yana faruwa kan masarautar Kano, inda mutum biyu ke ikirarin kasancewa halastattun sarakuna.

 

Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’amuran Cikin Gida na jihar, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya bayyana hakan a ranar Alhamis, inda ya ce gwamnati ta tsara abubuwa na musamman domin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a gidan sarautar.

 

Kusan shekaru biyu kenan Kano na fama da rikicin sarauta, inda Sarki Muhammadu Sanusi II ke zaune a fadar Gidan Rumfa, yayin da Sarki Aminu Ado Bayero ke zaune a fadar Nassarawa ƙarƙashin tsaron jami’an gwamnatin tarayya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Kanwan Katsina Advocates Establishment of FM Stations Across 3 Senatorial Zones Katsina

The Kanwan Katsina District Head of Ketare, Alhaji Usman Bello Kankara mni, has emphasized the need for continuous training and capacity building for journalists, particularly...

‎Ganduje Ba Shi da Alhakin Sace Dadiyata – Shehu Sani

Tsohon dan majalisar dattawa mai wakiltar mazabar Kaduna ta Tsakiya a Majalisar Dattawa ta 8, Shehu Sani, ya karyata zargin da tsohon gwamnan Jihar Kaduna,...

Most Popular