HomeSashen HausaJami’an da Aka Kama Kan Yunkurin Juyin Mulki Za Su Ɗanɗana Kuɗarsu–...

Jami’an da Aka Kama Kan Yunkurin Juyin Mulki Za Su Ɗanɗana Kuɗarsu– Ministan Tsaro 

-

Ministan tsaron Najeriya, Christopher Musa, ya ce jami’an sojojin da aka kama bisa zargin yunkurin juyin mulki da aka dakile sun san sakamakon abin da suka aikata.

 

An kama jami’an sojoji 16, ciki har da birgediya janar da kanar, a watan Oktoban 2025. Daga bisani, Hedikwatar Tsaro ta tabbatar da cewa, an gano shirin kifar da Shugaba Bola Tinubu, wanda aka ce an gano shi ne ta hanyar haɗin gwiwar bayanan sirri daga sojoji, DSS da DIA.

 

Da yake magana a wata hira da ya yi da TRT World, Musa ya tabbatar da cewa, za a yi wa waɗanda ake zargi shari’a cikin adalci, tare da ba su damar ɗaukar lauya.

 

Haka kuma, ya ce gwamnati za ta kula da iyalan jami’an da ake zargi.

 

Musa ya jaddada cewa masu hannu a yunkurin sun riga sun san illar abin da suka aikata, kuma suna shirye su fuskanci hukuncin da doka ta tanada.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Kanwan Katsina Advocates Establishment of FM Stations Across 3 Senatorial Zones Katsina

The Kanwan Katsina District Head of Ketare, Alhaji Usman Bello Kankara mni, has emphasized the need for continuous training and capacity building for journalists, particularly...

‎Ganduje Ba Shi da Alhakin Sace Dadiyata – Shehu Sani

Tsohon dan majalisar dattawa mai wakiltar mazabar Kaduna ta Tsakiya a Majalisar Dattawa ta 8, Shehu Sani, ya karyata zargin da tsohon gwamnan Jihar Kaduna,...

Most Popular