Rahotanni daga jihar Katsina sun tabbatar da cewa wasu ’yan bindiga sun kai hari a unguwar Sabon Layi da ke gundumar Kakumi, a karamar hukumar Bakori, inda suka sace akalla mutane 15 ciki har da mata da kananan yara.
An ruwaito cewa harin ya faru ne da misalin karfe 9:45 na daren ranar Alhamis, kamar yadda wata majiya ta bayyana. Rahoton ya nuna cewa maharan sun kai farmaki gidaje biyu, inda suka tafi da mutanen ba tare da yin harbi ba, domin kauce wa jan hankalin jama’a.
Majiyoyi sun kara da cewa ’yan bindigar sun rabu gida biyu yayin harin; wasu daga cikinsu na satar shanu domin karkatar da hankalin mazauna yankin, yayin da sauran suka kutsa cikin unguwar suka aiwatar da sace-sacen.
Bayan harin, mazauna yankin tare da hadin gwiwar ’yan sa-kai sun yi yunkurin bin sawun maharan domin ceto wadanda aka sace, sai dai ba a samu nasara ba.
Haka kuma, akwai zargin cewa wani da ake kira Kwashen Garwa na iya kasancewa yana da hannu a lamarin, duk da cewa an taba kulla yarjejeniyar sulhu da shi a baya.
A wani bangare kuma, an ce ’yan bindiga sun kakaba harajin naira miliyan 10 kan wasu kauyuka a kananan hukumomin Bakori da Faskari, tare da gargadin manoma da kada su fara noma har sai sun biya kudin.
Mazauna yankunan sun nuna damuwa kan yadda matsalar tsaro ke kara tsananta, suna kira ga gwamnati da ta dauki matakan gaggawa domin dakile irin wadannan hare-hare.
Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, babu wata sanarwa a hukumance daga jami’an tsaro dangane da lamarin.
