HomeSashen HausaAn Rufe Jama'ar UMYUK Katsina Sai Baba Ta Gani

An Rufe Jama’ar UMYUK Katsina Sai Baba Ta Gani

-

An Rufe Jama’ar UMYUK Katsina Sai Baba Ta Gani

 

Kungiyoyin Malamai da ma’aikatan Jami’ar Ummaru Musa Yar’adua (UMYU) a Katsina sun tsunduma yajin aiki “sai baba ta gani” a ranar Litinin, 3 ga watan Nuwamba 2025.

 

Rahotanni sun bayyana cewa, yajin aikin ya shafi dukkan Malamai da ma’aikatan jami’ar, sakamakon wasu matsalolin da suke zargin gwamnati ta yi biris da su. Daga cikin korafe-korafen da suka gabatar sun hada da; Rashin ingantaccen jin daɗin ma’aikatan jami’ar, Matsalar kwace ikon gudanar da shafin (portal) na makaranta.

 

Sauran sun hada da Karancin kuɗaɗen gudanarwa, da kuma batun walwalar Ɗalibai.

 

Sai dai a nata ɓangaren, Gwamnatin Jihar Katsina ta yi watsi da korafe-korafen kungiyar, tare da jaddada cewa, tana ci gaba da ƙoƙarin magance dukkan matsalolin da suka shafi jami’ar da cigaban ilimi a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

NSCDC Ta Tura Jami’ai 1,256 A Jihar Katsina, Don Kare Muhimman Kadarorin Kasa Da Ababen More Rayuwa

A wani mataki na musamman domin tabbatar da isasshen tsaro, Kwamandan NSCDC na Jihar Katsina, AD Moriki, ANIM, ya amince da tura jami’ai 1,256 domin...

‎‘Yansanda Sun Jaddada Ƙara Matakan Tsaro Yayin Bukukuwan Kirsimeti

‎Yayin da ‘yan Najeriya ke shirin shiga bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara, Shugaban Rundunar ‘Yan Sanda ta Ƙasa, IGP Kayode Adeolu Egbetokun, ya ba da...

Most Popular