HomeSashen HausaFulani Na Ƙoƙarin Ƙwace Garuruwa Da Kuma Gonaki A Yankin Dukku Da...

Fulani Na Ƙoƙarin Ƙwace Garuruwa Da Kuma Gonaki A Yankin Dukku Da Darazo A Jihar Gombe

-

Rahotannin sun bayyana cewa, wasu Fulani suna ƙoƙarin ƙwace wasu garuruwa da ke tsakanin kan iyakar ƙananan hukumomin Dukku (Jihar Gombe) da Darazo (Jihar Bauchi).

Shaidun gani da ido da suka fito daga yankin, su ne suka tabbatar da faruwar lamarin, inda suka ce, fulanin sun tarwatsa al’ummar garin Yau Tare, inda suka ka umarce su da su gaggauta barin garin.

Kamar yadda Nigerian Post ta bibiyi rahoton, dalilin hakan ne ya sa ma zauna garin suka fara ƙaura nan take, bayan sun kashe wani a yayin da suka kai hari garin.

Haka zalika, sun shiga wasu garuruwa kamar Jamari, Dukkuyel a ranakun Kasuwa, inda suka dinga dukkan mutane babu wani dalili.

Tuni dai aka tabbatar da faruwar lamarin, inda aka kara jaddada cewa, Fulanin na yawo tsakanin Yau Tare, Hashidu, Malala, Jamari Dukkuyel da wasu garuruwa, wanda hakan ya jefa al’umma cikin tashin hankali da gudun hijira.

Haka zalika, sun bayyana aniyarsu ta amfani da gonakin al’ummar yankin, lamarin da ya ƙara tayar da hankalin manoma da iyalai.

Rahotanni kuma na cewa, ana zargin Fulanin da gayyato abokan su daga wasu sassa daban-daban na ƙasar nan domin ƙara ƙarfi, yanzu haka sun sauka cikin dajin Darazo.

Saboda haka ake kira ga gwamnatocin jihohin Gombe da Bauchi da su gaggauta ɗaukar mataki na musamman, domin kare rayuka, gonaki da dukiyoyin jama’a a wannan yanki kafin lamura su rikide zuwa rikicin da zai fi ƙarfin Gwamnati.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina Police Received 29 New ASPs From The Nigeria Police Academy, Wudil

The Katsina State Police Command has received 29 newly posted Assistant Superintendents of Police (ASPs) from the Nigeria Police Academy, Wudil. Welcoming the officers, the...

Yawancin Fulanin Da Suke Ta’addanci Ba Su Da Addini, Ba Su San Allah Ba– Nasir El Rufa’i ‎

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufa’i, ya bayyana cewa yawancin mutanen Fulani da ake zargi da aikata ta'addanci da kashe kashe a sassa daban...

Most Popular