HomeSashen Hausa‎Malami Ya Zargi DSS da Tauye Masa ’Yancin Kare Kansa a Kotu

‎Malami Ya Zargi DSS da Tauye Masa ’Yancin Kare Kansa a Kotu

-

‎Tsohon Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya, Abubakar Malami (SAN), ya zargi Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) da daukar matakan hana shi cikakken ’yancinsa na shari’a da kare kansa yadda doka ta tanada.

‎A cikin wata sanarwa da Mai Taimaka Masa kan Harkokin Yaɗa Labarai, Mohammed Bello Doka, ya sanya wa hannu, Malami ya ce DSS na ci gaba da hana lauyoyinsa damar ganinsa, lamarin da ya hana shi tuntuba, ba da umarni, da kuma shirya takardun shari’a yadda ya dace.

‎Malami ya bayyana hakan a matsayin tauye hakkokin ɗan Adam, yana mai cewa irin waɗannan matakai sun sabawa tanade-tanaden kundin tsarin mulkin Najeriya.

‎“Abin da ke faruwa ya nuna wani salo da ake fara kama mutum kafin bincike, sannan a fara neman hujjoji bayan tsare shi, wanda hakan ya saɓa doka da kuma ’yancin da kundin tsarin mulki ya tanada,” in ji sanarwar.

‎Ya ƙara da cewa abin damuwa ne matuƙa ganin yadda DSS ke aiwatar da abin da ya kira tsarewa, sannan neman hujjoji daga baya, yana mai jaddada cewa hakan barazana ce ga bin doka da oda ta ƙasa.

‎Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, DSS ba ta fitar da wata sanarwar martani kan zargin da tsohon Ministan ya yi ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎An Cafke Wani Mutum Da Zargin Sayar Da Jaririn ‘Yar’ uwarsa Naira Miliyan 2 a Legas

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta kama wani mutum mai shekaru 30 da haihuwa bisa zargin sayar da jaririn ‘yar uwarsa mai wata daya kacal...

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi Hukumar tsaron farin kaya ta DSS sun damƙa matashiya Walida Abdullahi Ibrahim ga Gwamnan Jihar Jigawa,...

Most Popular